Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majo Hamza Al-Mustapha Ya Koma Gidanshi A Kano


Wani dangin Maj. Hamza Al-Mustapha yana kuka bayan hukumcin da aka yanke a Lagos bara
Wani dangin Maj. Hamza Al-Mustapha yana kuka bayan hukumcin da aka yanke a Lagos bara

Dubban magoya baya, da 'yan'uwa da abokan arzikin Majo Al-Mustapha sun yi mashi gagarumar tarba a birnin Kano

Dubban masoya, ‘yan’uwa da abokan arziki sun yi dafifi a tashar jirgin saman kasa da kasa na Aminu Kano dake birnin Kano jiya domin tarbar Majo Hamza Al-Mustapha wanda kotun daukaka kara ta wanke bayan ya shafe shekaru goma sha hudu a gidan yari bisa zargin kashe Kudirat Abiola matar tsohon hamshakin dan kasuwan da aka kyautata zaton shine ya lashe zaben shekara ta dubu da dari tara da casa’in da uku.

Bayan saukarsa daga jirgi kafin isarsa zuwa gida, Majo Hamza Al-Mustapha ya fara yada zango a gidan gwamnatin jihar Kano da fadar Sarkin Kano da kuma gidan tsohon shugaban Najeriya, marigayi Sani Abacha inda ya kai gaisuwar bangirma, daga nan ya wuce makabartar kofar Mazugal inda aka yi addu’a ta musamman ga mahaifansa da aka binne a can.

Daga bisani Majo Hamza Al-Mustapha ya yi jawabi ga dumbim wadanda suka fito tarbarshi a kofar gidanshi dake Lamido Rod a birnin Kano.

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:02 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG