Messi dan kasar Argentina, zai karkare kwantaraginsa a Barcelona a bazara mai zuwa, inda kuma alamun ficewar kungiyar daga gasar Zakarun Turai da wuri, ya kara uzzura rade-radin cewa zai bar kungiyar.
To sai dai akwai rashin tabbas sakamakon zaben da ake gudanarwa na shugabancin kungiyar ta Barcelona, a yayin da dukkan ‘yan takara 3 na mukamin suka bayyana kudurinsu na ci gaba da rike dan wasan.
Messi mai shekaru 33 da haihuwa, ya lashe lambar gwarzon dan kwallon duniya ta Ballon D'Or har sau 6.
An dade ana rade-radin yiwuwar komawar sa a kungiyar City musamman saboda dangantakar sa da tsohon kocinsa Pep Guardiola, duk da yake kuma wasu rahotannin na cewa kungiyar Paris St-Germain ta kasar Faransa ma tana sha’awarsa.
An ba da rahoton cewa City ta yi tayin dan wasan da ihsani mai tsoka, to amma kuma kungiyar ta ce ba gaskiya ba ne, ba wani tayi da ta yi wa Messi a yanzu da ma can baya.
Messi ya bukaci barin Barcelona a watan Agustan shekarar da ta gabata, to amma kuma shugaban kungiyar na wannan lokacin Josep Maria Bartomeu ya toshe kafar tafiya ga dan wasan.