Wannan dama ta hawa teburin gasar ita ce ta farko da kungiyar ta samu tun bayan kakar wasa ta 2012-13 a lokacin kungiyar na karkashin kulawar Sir Alex Ferguson.
Kwallon da Paul Pogba ya zira ce ta kai Man U ga wannan nasara bayan da aka dawo daga hutun rabin lokaci.
Hakan kuma ya ba kungiyar damar samun maki ukun da ya sa kungiyar ta yi wa sauran kungiyoyin zarra a teburin gasar.
An dai kwashe zangon farko na wasan ba tare da an zira wata kwallo ba amma da aka dawo daga hutun rabin lokaci a daidai minti na 71, Pogba, ya zira kwallo a ragar Burnley.
Manchester na da maki 36, sai Liverpool da ke biye da ita da maki 33 sai kuma Leicester mai maki 32 a teburin.
A ranar 17 ga watan Janairu Liverpool za ta kara da Manchester United a wasan da ake ganin zai yi zafi.
Leicester za ta kara da Southampton, sai kuma Sheffiled United ta karbi bakunci Tottenham.
Dubi ra’ayoyi
Ko ka yi rijista da mu? Shiga shafinka
Ba ka yi rijista da mu ba? Yi rijista
Load more comments