Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Marwa Na So A Rika Yi wa Daliban Jami’a Gwajin Amfani Da Miyagun Kwayoyi


Shugaban NDLEA, Muhammad Buba Marwa (Twitter/ NDLEA)
Shugaban NDLEA, Muhammad Buba Marwa (Twitter/ NDLEA)

Shugaban hukumar da ke yaki da amfani da miyagun kwayoyi ta NDLEA, Janar Buba Marwa mai ritaya, ya yi kira da a samar da wani tsari da za a rika yi wa daliban jami’a da sauran manyan makarantu gwajin da zai tantance ko suna tu’ammuli da miyagun kwayoyi ko akasin hakan.

Hukumar ta NDLEA ta ce akwai bukatar a samar da wannan tsari ba a jami’o’i kadai ba, har ma da sauran manyan makarantun gaba da sakandare.

Marwa ya yi kiran ne yayin kaddamar da wani shirin yaki da amfani da miyagun kwayoyi a Jami’ar Abuja a ranar Laraba.

Shugaban na NDLEA ya ce akwai bukatar a hada kai tsakanin hukumar da jami’o’in Najeriya ta yadda za a kafa ofisoshi a cikin makarantun don karfafa yaki da wannan mummunar dabi’a

Tsarin na gwajin zai hada da tsoffi da sabbin dalibai da za a diba a makarantun a cewar shugaban hukumar ta NDLEA.

Marwa ya kara da cewa, matsalar amfani da miyagun kwayoyi ta zama babban abin damuwa a Najeriya musamman a tsakanin matasa.

XS
SM
MD
LG