Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

MDD: Ba A Rajistar Haihuwar Yara Kanana A Nahiyar Afirka


Majalisar Dinkin Duniya ta ce, kusan rabin daukacin adadin kananan yara a nahiyar Afirka ba a yi musu rijista ba a lokacin haihuwarsu, abin da ta ce na shafar damar da suke da ita ta kai wa ga wasu ababan more rayuwa, kamar na kiwon lafiya da kiwon lafiya.

Majalisar ta kuma ce matsalar, ta fi kamari ne a yankunan karkara, inda ake haifar yara a gida, ba tare da iyayensu sun je sun yi musu rijista ba.

An dago wannan batun ne a gefen taron ministocin kasashen Afirka da fannin yin rijistar yara ke karkashin ma’aikatunsu, wanda yake gudana a Zambia.

A cewar wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya a yankin Zambia, Coumbia Mar Gado, rashin yin rijistar na yin mummunan tasiri wajen ginawa yaran rayuwa mai inganci.

Ta kara da cewa, “idan ba ka yi wa yaranka rijista ba, tamkar ba a san da zamansa ba ne, a kasashen Afirka da dama, ba za ka iya saka yaranka a makaranta ba idan ba shi da rijistar haihuwa.”

Facebook Forum

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG