WASHINGTON D.C. —
Babban Sakataran Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya ce an samu gagarumin ci gaba a dangantakar da ke tsakanin Majalisar ta Dinkin Duniya da kungiyar tarayyar Afirka ta AU.
Inda ya yi fatan hakan zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da ke addabar nahiyar.
Guterres ya ce, Burinmu shi ne, mu taimakawa nahiyar Afirka ta shawo kan matsalolinta, ta yadda za a daina yiwa nahiyar kallon mai cike da dumbin matsaloli.
Sannan ya kuma yi nuni da yadda aka shawo kan rikicin Jamhuriyar Afrika ta tsakiya.
Yayin da kungiyoyi masu dauke da makamai, suka cimma wata matsaya a Sudan, kan kawo karshen rikicin kasar, wanda aka kwashe shekaru biyar ana yi.
Za ku iya son wannan ma
-
Maris 27, 2023
Mataimakiyar Shugaban Amurka Ta Fara Ziyarar Aiki A Ghana
-
Maris 26, 2023
Mataimakiyar Shugaban Amurka Kamala Harris Ta Isa Ghana
-
Maris 20, 2023
Ranar Farin Ciki Ta Duniya
Facebook Forum