Shaidun gani da ido sun bada labarin cewa harbe-harben da aka rika yi da igogi a Mogadishu, babban birnin kasar Somalia yayi sanadiyyar mutuwar mutane akalla bakwai.
Shaidun gani da idon sun bayyana haka ne Safaiyar yau Talata, kuma anyi harbe-harebn a da tsakar dare. Daga cikin wadanda suka halaka a dalilin harbe-harben harda wasu iyalai da ‘ya’yansu biyu.
Harkokin tsaro sun fara ingantuwa a birnin Mogadishu tun daga lokacin da hadin gwiwar sojin Somaliya da na kungiyar tarayyar Afirka suka sami nasarar korar mayakan al-shabab daga birnin Mogadishun.
Amma duk da haka ana ci gaba da samun harbe-harbe jifa-jifa, da suka hada harda makaman roka.
Gwamnatin rikon Somalia na samun goyon bayan rundunar sojin tarayyar Afirka kuma a watan Fabarairun da aya gabata ne suka sami nasarar korar mayakan al-Shabab daga birnin Mogadishu.