Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mutanen Timbuktu Sun Fara Tayar Da Kayar Baya Ma 'Yan Ansar Dine


Ma'aikata a daya daga cikin Masallatai masu tarihi na Timbuktu a kasar Mali
Ma'aikata a daya daga cikin Masallatai masu tarihi na Timbuktu a kasar Mali

Shaidu sun fadawa VOA cewa ‘yan zanga-zanga sun kewaye wani masallacin garin suka hana ‘yan kishin addini shiga ciki don sallar Jumma’a.

Mazauna yankin Timbuktu dake arewacin kasar mali sun fara tayar da kayar baya ma ‘yan kishin Islama dake kokarin shimfida tsarin shari’a a yankin.

Shaidu a garin Goundam sun ce an fara tayar da kayar bayar ne a lokacin da ‘yan kishin addini na kungiyar Ansar Dine suka daki wata matar da ba ta rufe kanta ba a jiya jumma’a. Suka ce jaririn da matar take dauke da shi ya ji rauni a lokacin da aka far mata.

Shaidu sun fadawa VOA cewa ‘yan zanga-zanga sun kewaye wani masallacin garin suka hana ‘yan kishin addini shiga ciki don sallar Jumma’a.

Suka ce masu kishin addinin sun yi ta harbi a sama domin tarwatsa mutanen da suka taru. Wani mazaunin garin ya fadawa VOA cewa yanzu dai kura ta lafa, koda yake akwai zaman dar-dar.

Garin Goundam yana cikin yankin da ‘yan awaren Abzinawa da masu kishin Islama suka kwace a karshen watan Maris, kuma a yanzu garin baki dayansa yana hannun masu kishin addini, ciki har da na kungiyar Ansar Dine.

Ansar dine ta ce tana son kafa tsarin shari’ar islama a fadin kasar Mali. A cikin ‘yan makonnin nan, kungiyar ta yi ta rusawa tare da lalata hubbaren wasu shaihunan malamai na Sufi a Timbuktu tana mai cewa barinsu sabo ne.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG