Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mutum 210 Cutar COVID-19 Ta Harba a Najeriya


Wasu ma'aikatan lafiya da ke kula da masu fama da cutar coronavirus
Wasu ma'aikatan lafiya da ke kula da masu fama da cutar coronavirus

Mutum 210 suka kamu da cutar coronavirus a Najeriya a cewar hukumar da ke kare yaduwar cututtuka ta NCDC a kasar.

Adadin ya kai haka ne, bayan da aka samu karin mutum 26 da cutar ta harba a kasar kamar yadda NCDC ta sabunta alkalumanta a shafinta na yanar gizo a ranar Juma’a.

“Daga cikin mutum 26; 11 a jihar Legas suke, takwas a Osun, uku a Abuja, uku a Edo sannan daya a Ondo.”

Amma duka sabbin mutanen da suka kamu da cutar, ba su nuna wata zazzafar alamar cutar ba, a cewar NCDC.

Hukumar ta kuma ce ya zuwa yanzu, mutum hudu ne suka mutu sanadiyyar cutar sannan an sallami wasu 25 bayan da suka samu sauki.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG