Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mutum Miliyan 48 Na Fuskantar Barazanar Yunwa A Yammacin Afirka - MDD


Wata mata da 'ya'yanta a gadon asibiti (AP)
Wata mata da 'ya'yanta a gadon asibiti (AP)

Jami’an Majalisar Dinkin Duniya sun ce matsalar yunwa na ci gaba da karuwa a yankin Yammacin nahiyar Afirka.

A cewar jami’an, mutum miliyan 48 ne suke fuskantar barazanar yunwa, musamman a yankunan da ke fama da rikice-rikice.

Jami’an sun bayyana hakan ne a Dakar, babban birnin Senegal a ranar Talata yayin wani taro da suka yi, inda suka ce matsalar ta samo asali ne daga rikice-rikice da annobar COVID-19 da kuma matsalar hauhawar farashin kayayyaki.

A cewarsu, kasashen da lamarin ya shafa sun hada da Burkina Faso, Mali, Niger, Arewacin Najeriya da kuma Mauritania.

Akalla mutum dubu 45 ne suke gab da fadawa kangin matsalar matsananciyar yunwa a yankin Sahel kamar yadda jami’an suka bayyana, adadin da ya zamanto sabon abu a yankin.

XS
SM
MD
LG