Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mutumin Da Ya Bude Wuta Kan Dalibai A Amurka Na Auna Kristoci Ne


Oregon School Shooting
Oregon School Shooting

Shedun da suka ga farmakin da aka kai a wata makarantar koleji dake jihar Oregon ta nan Amurka, sunce wanda ya kai harin na jiya Alhamis har ya kashe mutane 9, yana auna Kiristoci ne kacokan.

Jami’ai sunce mutumin da ya kai harin, wanda yazo dauke da makamai da yawa a jikinsa, ya kunna kai a wannan kolejin ta Umpqua da hantsi ne, inda ya shiga bude wuta kai tsaye.

Daga baya shima ya rasa nashi ran a musayar wutar da yayi da ‘yansanda.

Akalla shedu biyu sunce mutumin, wanda har yanzu ba’a bada sunanshi ba, ya tambayi biyu daga cikin mutanen da ya kashe ko idan su Kiristoci ne kafin ya bindige su har Lahira.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG