Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

NAHCON Ta Rufe Karbar Kudin Kujerar Aikin Hajjin Bana


Hukumar alhazan Najeriya NAHCON za ta rufe karbar kudin kujerar aikin hajjin bana daga Litinin din nan 15 ga watan nan na Yuli matukar dai tsarin bai sauya ba.

Wannan ma ya biyo bayan kara wa’adin lokaci ne na biyan kudin bayan samun wani ragi a farashin kujerar da fiye da Naira dubu 50.

Shugaban hukumar alhazan Barista Abdullahi Mukhtar Muhammed, ya ce za a kammala amsar kudin don samarwa dukkan maniyyatan izinin tafiya “VISA” don gudanar da aikin hajjin.

Tun ranar Laraba 10 ga watan nan a ka kaddamar da fara jigilar alhazan daga jihar Katsina, inda wasu yankunan ma kamar Kaduna rukunin alhazan su ka sauka a Saudiyya.

Malamai na kan gaba a lamarin na aikin hajji don kula da nunawa maniyyatan dokokin aikin a aikace don gudun samun cikas.

Jami’in hukumar alhazan Umar Bala da tuni ya ke Madina ya shaidawa muryar Amurka yadda a ka tsara malaman za su kasance da alhazai a kowanne waje na sauke faralin.

Zuwa yanzu kimanin alhazai 5000 sun sauka a Saudiyya cikin kimanin alhazan Najeriya 65,000 da a ke sa ran za su gudanar da aikin hajjin na bana.

Domin Karin bayani saurari rahotan Nasiru Adamu El-Hikaya.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:55 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG