Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce yankin nahiyar turai ya wuce China a matsayin yankin da cutar coronavirus ta fi addaba a duniya.
A jiya Juma’a shugaban hukumar Tedros Ghebereyesus ya fadawa manema labarai a birnin Geneva cewa, ana ci gaba da samun karin wadanda ke kamuwa da cutar a kullum sama da abin da aka gani a China a lokacin da cutar ta tashen bazuwa.
Kasar Italiya ta bayyana a jiya Juma’ar cewa, adadin wadanda suka kamu da cutar ya karu da mutum dubu 2,500 cikin sa’o’i 24 da suka gabata, abin da ya kai jimillar masu dauke da cutar a kasar zuwa 17,660.
Duk da cewa, Burtaniya ba ta cikin kasashen da Shugaba Trump ya haramtawa shiga Amurka, akwai daruruwan mutane da suka kamu da cutar a kasar da ma Ireland.
Hakan ya sa Firai Minista Boris Johnson ya fito baro-baro ya fadawa al'umar kasar gaskiya.
“Ya zama dole na fadawa al’umar Burtaniya gaskiya, iyalai da dama za su rasa masoyansu tun kafin wa’adinsu ya yi.” In ji Johnson.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus