Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya da Kuwait Zasu Shiga Yarjeniyoyi


Sarkin Kuwait Sheikh Sabah al-Ahmad al-Sabah
Sarkin Kuwait Sheikh Sabah al-Ahmad al-Sabah

A karo na farko tunda Najeriya da Kuwait suka kafa dankon diflomasiya tsakaninsu shekaru 33 da suka gabata, kasashen zasu shiga wasu yarjeniyoyi.

Bayan sun kwashe shekaru 33 suna hullda ta diflomasiya tare Najeriya da Kuwait zasu kulla wasu yarjeniyoyi.

Yarjeniyoyin da Najeriya zata kulla da kasar Kuwait zasu taimaka wurin samar da aikin yi da inganta harkokin kasuwanci. Jakadan Najeriya a kasar Kuwait Ambassador Haruna Garba yace Najeriya zata kulla yarjeniyoyi shida da kasar.

Tun shekarar 1981 aka bude ofishin jakadancin Najeriya a Kuwait wadda kasa ce karama amma tana da karfin tattalin arziki.

Kawo yanzu dai akwai 'yan Najeriya a fannin ilimin kasar ta Kuwait suna koyaswa da wasu kuma dake kasuwanci. Ban da haka 'yan Najeriya da yawa suna da ajiya a kasar ta Kuwait. Yanzu dai akwai 'yan Najeriya kusan dubu biyu da dari biyar mazauna Kuwait.

Yarjeniyoyi shidan da zasu kulla sun hada da zirga-zirgar jiragen sama tsakanin kasashen biyu da na kasuwanci da dai sauransu.

Ga rahoton Sa'adatu Fawu.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG