Rahoton baya-baya na cibiyar kula da cututtuka masu yaduwa ta Najeriya NCDC ya nuna cewa an samu sabbin mutum 242 da suka kamu da cutar coronavirus.
Hakan ya sa gaba dayan adadin wadanda cutar ta harba a kasar yanzu ya kai dubu hudu da dari shida da arba'in da daya. 4,641
Jihohin da aka samu karuwar masu cutar sun hada da Legas inda mutuum 88 suka harbu, 64 a Kano, 49 a Katsina, 13 a Kaduna, tara a Ogun, shida a Gombe, hudu a Adamawa, sai kuma birnin tarayya Abuja inda aka samu mutum uku.
An samu karin mutum daya-daya a jihohin Ondo, Oyo, Rivers, Zamfara, Borno da kuma Bauchi da cutar ta kama.
Ya zuwa daren ranar Litinin 11 ga watan Mayu, mutum 902 ne suka warke daga cutar a kasar, yayin da mutum 150 suka rasa rayukansu sakamakon cutar.
Za ku iya son wannan ma
-
Maris 08, 2021
Ranar Mata Ta Duniya: Mata A Jihar Borno Na Neman Dauki
-
Maris 08, 2021
Mata Suna Neman Gwamanati Ta Dama Da Su
-
Maris 07, 2021
Ba Bu Wanda Yake So Najeriya Ta Rabu - NOA
-
Maris 07, 2021
Masu Garkuwa Ku Taimaka Ku Ba Mu Gawar Dan-uwanmu - Dangi
Facebook Forum