Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nan Ba Da Jimawa Ba Za A Sake Bude Filin Jirgin Saman Kano


Filin Jirgin Saman Mallam Aminu Kano 1
Filin Jirgin Saman Mallam Aminu Kano 1

Ana gab da kammala shirye-shiryen bude tashar jiragen sama ta kasa-da-kasa da ke Kano.

Yunkurin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, na ganin an sake bude ayyukan jigilar fasinjoji na kasa-da-kasa a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano, da filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ake cigaba da aiki a kai don bunkasar tattalin arzikin jihar Kano, ya kusa yiwuwa.

Shi ma, Ministan sufurin jiragen saman Najeriya, Hadi Sirika, ya bayyana cewa, tattaunawa a kan sake bude zirga-zirgar kasa da kasa a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano, da sabon filin jirgin saman kasa-da-kasa na Murtala Muhammad, ta yi armashi.

Game da batun ba wa masu zuba jari daga ciki da wajen Najeriya damar shiga a dama da su, wajen bunkasa fannin sufurin jiragen saman Najeriya, Sirika ya ce. "Wannan gwamnatin ba za ta saida kaddarorin al'umma ba, kamar yadda aka yi a baya, za dai a bada su a matsayin jingina, a kuma bunkasa su, daga baya su kuma cigaba da zama mallakar kasa."

Sake bude zirga-zirgar jirgin saman kasa da kasa a Kano zai yi matukar tasiri ga tattalin arzikin Najeriya in ji Jamil Yunusa. "musamman idan aka yi la'akari da irin hada-hadar da ake samu a jihar."

Ga rahoton Halima Abdulra’uf a cikin sauti.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:30 0:00

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Wata manhaja mai saukaka wahalar samun gidan abinci na halal ga Musulman dake zaune a kasashen Turai
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:21 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG