Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

NATO ta kai hari Libya da rana


Hayaki a sararin samaniyar birnin Tripoli, Libya bayan da kungiyar Nato ta kai hari.
Hayaki a sararin samaniyar birnin Tripoli, Libya bayan da kungiyar Nato ta kai hari.

A yau asabar din nan tashin bama bamai suka girgiza birnin Tripoli a yayinda kungiyar kawancen tsaro ta NATO ta kai hare haren ba saban ba da rana. Kungiyar NATO tace ta auna wata motar adana na tafi da gidanka a wani gida da a wasu lokutan shugaba Gaddafi yana zama a cikinsa.

A yau asabar din nan tashin bama bamai suka girgiza birnin Tripoli a yayinda kungiyar kawancen tsaro ta NATO ta kai hare haren ba saban ba da rana. Kungiyar NATO tace ta auna wata motar adana na tafi da gidanka a wani gida da a wasu lokutan shugaba Gaddafi yana zama a cikinsa. Kamfanin dilanci labarun Faransa ya bada labarin cewa ana gani hayaki na tashi daga inda bam din ya fashe. Tunda farko a yau asabar hare haren da NATO ta kai sun haskaka sararin samaniyar birnin Tripoli. A halin da ake ciki kuma, kasar Rasha wadda daddiyar kawar Libya ce, tayi tayin shiga tsakani a kula yarjejeniyar da zata sa shugaba Gaddafi ya sauka daga ragamar mulki. Shugaban Rasha yace shugaba Gaddafi zai sauka daga kan ragamar mulki. Shugaban na Rasha yayi wannan furucin ne a jiya juma’a a karshen taron kolin kungiyar kasashe masu arzikin masana’antu a kasar Faransa inda kuma ya bada sanarwar cewa zai tura wani wakilinsa zuwa birnin Benghazi, babar tungar yan tawaye. Tunda farko a jiya juma’a sojojin dake biyaya ga shugaba Gaddafi sun sabunta yunkurin sake kwato birnin Misrata wanda ke hanun yan tawaye. Bangarorin biyu sun fafata a unguwani da dama na birnin.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG