Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Neymar Zai Sabunta Kwantiraginsa Da PSG


Neymar, dan wasan PSG
Neymar, dan wasan PSG

Dan wasan Brazil Neymar da ke taka kwallo a kungiyar PSG ta kasar Faransa, yana kan tattaunawa da hukumomin kungiyar don ganin yadda zai tsawaita zamansa a kungiyar.

Bayanai sun yi nuni da cewa Neymar, dan shekara 28, na jin dadin zamansa a club din saboda haka yana shirin sabunta kwantiraginsa.

A watan Yunin shekara mai zuwa kwantiraginsa zai kare wanda ya saka hannu a shekarar 2017 a lokacin da ya yi kaura daga Barcelona akan pam miliyan 200

A da, an yi ta yamadidin Neymar zai koma Barcelona a lokacin da aka dan bude kasuwar ‘yan wasa a watan Yunin 2019, amma yanzu bayanai sun yi nuni da cewa zai yi zamansa a Faransa.

A watan Disamba, shugaban kungiyar Nasser Al-Khelaifi, ya ce suna da kwarin gwiwar Neymar da Kylian Mbape za su ci gaba da zama a PSG.

A lokacin da ya yi ruwan kwallo uku a wasan karshe na gasar zakarun turai tsakanin PSG da Istanbul Basaksehir a watan Disamba, Neymar ya jaddada sha’awarsa ta ci gaba da zama a Paris.

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG