Hukumar wanzar da zaman lafiya da sasanta al’umma a jahar Pilato ta shirya taron bita wa ‘yan jarida kan yadda zasu gudanar da aikinsu da zai taimaka wajen samar da zaman lafiya, maimakon ruruta wutar rikici.
Taron bitar wanda ya sami tallafin ofishin jakadancin kasar Amurka a Najeriya, ya kara tunatar da ‘yan jarida daga kafofin watsa labarai na ciki da ketare kan muhimmancin hadin kan al’umma.
Shugaban hukumar wanzar da da zaman lafiya a jahar Pilato, Joseph Lengman yace ‘yan jarida na da gagarumin gudummowa wajen samadda zaman lafiya da bukasar kasa.
Mahalarta taron da Sashen Hausa ya yi hira da su sun bayyana cewa, sun karu sosai.
Saurari cikakken rahoton Zainab Babaji.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.