Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Paul Biya: Kodai Ku Ajiye Makamai Ko Ku Fuskanci Ukuba


Yankunan mutanen kasar Kamaru masu magana da harshen Ingilishi a kasar sun dai-daice, tun bayan wani farmaki da ‘yan sanda suka kai a yankin da yayi sanadiyar mutuwar mutane 30 a cikin kwanaki biyu.

Sabon fadan ya kaure ne kusan sati daya da rantsar da shugaba Paul Biya, wanda yayi gargadi ga ‘yan a ware da su ajiye makamansu, ko kuma a kashesu.

A yau Laraba ne mai magana da yawun rundunar sojojin kasar Colone Didier Bedjeck, ya fada cewa an samu karuwar mace-mace, biyo bayan arangama da aka samu na ‘yan kwanaki, inda yace yawan mutanen da aka kashen sun cira zuwa fiyeda 30.

Mai magana da yawun kungiyar ta ‘yan aware Ivo Tapng, kuma ya shaida ma kamfanin dillancin labarai na Reuters, cewar mayakansu biyu ne kawai suka mutu, amma su kuwa sun kashe sojoji gwmnati 13.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG