Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rahoton IMF Ya Nuna Damuwa Game Da Tsanantar Cin Hanci A Nijar


Wani rahoton binciken asusun bayar da lamani na IMF ko FMI, ya gano cewa cin hanci na kara ci gaba da zama a jamhuriyar Nijar, musamman a ma’aikatun gwamnati duk da irin matakan da hukumomin kasar ke dauka da nufin dakile wannan haramtaciyar dabi’a.

Rahoton wanda aka kammala a karshen watan Agusta da ya gabata, na kunshe da wasu bayanan da asusun bayar da lamani na FMI ya tattara bayan binciken da aka gudanar a sassa daban daban na jamhuriyar Nijar, lamarin dake fayyace zahirin halin da ake ciki akan maganar yaki da cin hanci a wannan kasa.

A hirar su da wakilin Muryar Amurka Souley Moumouni Barma, shugaban reshen transparency Malam Maman Wada ya kara haske akan wannan matsala, a bayanin sa.

Lokacin binciken na asusun IMF ya karkata akan kuri’ar jin ra’ayin jama’a game da yadda talakawa ke kallon batun cin hanci a Nijar.

Saboda haka zartar da doka akan dukkan wadanda aka tabbatar da samunsu da hannu a harkar cin hanci, ita kadai ce hanyar da za ta bada damar karya lagon masu aikata wannan haramtaciyar dabi’a.

Ga cikakken rahoton daga wakilin Muryar Amurka Souley Moumouni Barma.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:07 0:00


Facebook Forum

XS
SM
MD
LG