Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ranar Kula da Koshin Lafiyar Ma’aikata A Duniya


Yau ce ranar kula da koshin lafiyar ma’aikata a wuraren ayyukan su da kuma basu kariya daga kowace barazana, yayin da suke bakin aiki. Kungiyar kwadago ta duniya ce ta ware kowace ranar 28 ga watan Afrilu domin gudanar gangamin wayar da kai dangane da muhimmancin ranar.

Manufar kebe ranar itace tattaunawa tare da bitar matakan kare ma’aikata daga tsangwama da kuma tabbatar da koshin lafiyarsu a lokacin da suke bakin aiki.

Wani rahoto da kungiyar Kwadago ta duniya ta fitar ya nuna cewa kimanin ma’aikata maza da mata Miliyan 2 ne ke rasa rayukansu a kowacce shekara sanadiyar hadura masu nasaba da aiyukansu ko cutuka da suka dauka a bakin aiki.

Rahotan yace ana samun afkuwar hadura a guraren aiki a duniya baki daya har sau Miliyan 270, yayin da ma’aikata Miliyan 160 ke daukar cutuka daban daban a kowacce shekara.

Domin karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:33 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG