Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rikicin Burundi ya kusa kaiga tabarbarewar doka da oda kwatakwata


'Yansandan kasar na cigaba da harbe mutane
'Yansandan kasar na cigaba da harbe mutane

Shugaban hukumar kare hakkin dan dama a Majalisar Dinkin Duniya, ya yi gargadi game da karin tashe-tashen hankula da ake ci gaba da samu a Burundi, lamarin da ya ce na gab da haifar da rashin doka da oda a kasar.

Shugaban hukumar, Zeid Ra’ad Al Hussein, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a yau Juma’a, yana mai cewa wasu samame da jami’an tsaron kasar suka kai a ranar 11 ga watan Disamba akan ‘yan adawa, sun keta hakkin bil adama.

Ya kara da cewa rahotanni sun nuna cewa a lokacin samamen an yiwa mata fyade kana akwai bayanai da ke cewa an ga wasu manyan kaburbura da aka binne mutane a yankin.

Al Hussein ya kuma ce wannan rahoto ne da ke nuna alamun cewa an dauki hanyar fadawa rikicin kabilanci.

A ranar 12 ga watan Disamba, dakarun kasar ta Burundi suka bayyana cewa an kashe mutane 87 a Bujumbura, babban birnin kasar, bayan wani hari da su ka yi ikrarin an kai akan a wasu sansanoninsu.

Sai dai wadanda suka shaida lamarin a yankin, sun yi zargin cewa har gida jami’an tsaron suka bi mutanen suka kashe su.

XS
SM
MD
LG