WASHINGTON D.C. —
Pakistan ta ce dakarun India sun yi harbe-harbe a tsallaken yankin Kashmir da ke tsakanin iyakarta da India, wanda ake kira LOC a takaice, inda farar hula hudu suka mutu wani kuma ya jikkata.
Wata sanarwar da rundunar sojin Pakistan ta fitar da yammacin ranar Laraba ta ce India ta saba yarjejeniyar tsagaita wutar da bangarorin biyu suka amince da ita.
A cewar Pakistan Indiar ta tsiri harbe-harbe akan kauyukan da ke karkashin ikon Pakistan a yankin ba tare da wata tsokana ba.
Sanarwar ta kuma kara da cewa dakarun Pakistan sun maida martanin harbin da India ta yi.
Sai dai nan take dai jami’an India ba su yi wani bayani kan wannan lamari ba.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum