Rundunar sojan sama na Nigeria tabi sahun sauran bangarorin sojojin kasar domin samar da tsaro a kudancin kasar musamman kudu maso gabas.
Sanarwan dake dauke da sa hannun kakakin sojan saman kasar Manjo Janar Adetokunbo Adesanya tace yanzu haka an kai wa jami’an da zasu yi aiki wannan yankin kayan aiki, wadanda suka hada da wani jirgi kirar Alfa jet, wanda akace an tura domin ya samar wa sojojin da zasu yi wannan aiki kariya ta musamman.
Wasu daga cikin wuraren da wannan aikin zai shafa sun hada da yankin kudu maso gabashin Nigeria, da kuma yankin Niger Delta.
Ga L amido Abubakar Sokoto da karin bayani.
Facebook Forum