Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rundunar Tsaron Najeriya Ta Jaddada Niyyar Murkushe Boko Haram


Hotunan Mukadashin Sufeton Yan Sanda da Kwamandan Runudnar Tsaro Ta musamman A Maiduguri
Hotunan Mukadashin Sufeton Yan Sanda da Kwamandan Runudnar Tsaro Ta musamman A Maiduguri

Rundunar tsaron Najeriya ta bayyana cewa, a wannan karon gwamnati ta zage damtse da kara damarar ganin bayan kungiyar Boko Haram, da kuma tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a yankunan da ake fama da tashe tashen hankali sakamakon hare haren kungiyar Boko Haram

Rundunar tsaron ta bayyana haka ne yayin liyafar bukuwan sallah da aka shiryawa wadanda suke zaune a sansanan ‘yan gudun hijira na cikin gida.

A jawabinsa, kwamandan rundunan sojin sama na 153 dake Yola, Air Commodore Mohammed Yusufu, ya yaba rawar da babban hafsan sojin sama ke takawa dake zaburar da na kasa don fuskantar yan ta'adda.

Shima a nashi jawabin ga askarawan saman babban hafsan sojin saman Najeriya, Air Marshall Saddique Abubakar, yace gwamnati ta kuduri aniyar shawo kan wannan matsalar baki daya a wannan karon.

Yau dai fiye da shekaru goma ke nan da yan kungiyar Boko Haram ke kai hare hare a wasu sassan Najeriya da kuma wasu kasashen dake makwabtaka da Najeriyan, da ya zama sanadin asarar dubban rayuka baya ga wadanda ke gudun hijira da kuma asarar dukiya.

Saurari cikakken rahoton Ibrahim Abdul’aziz

Rundunar tsaro ta lashi takobin shawo kan Boko Haram-3:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG