Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rundunar 'Yan Sandan Najeriya Tana Farautar 'Yan Bangar Siyasa


'Yan Najeriya a wajen gangamin siyasa
'Yan Najeriya a wajen gangamin siyasa

Rundunar ‘yan sandan Najeriya tace tana ci gaba da farautar wasu da take tuhuma da hannu ga aikata laifukan da ke da alaka da tarwatsa zaman lafiyar al'umma da sunan murna akan samun nasarar zabe.

Wannan na zuwa ne bayan wasu mutane 781 da rundunar ta kama da laifuka a lokutan zabubuka a jihohi daban daban.

Mutanen da rundunar ta ce ta kama akan tuhumar aikata laifuka a lokutan zabe an kama su ne a jihohi daban daban kamar jihar Sokoto inda aka kama wadanda ke da hannu a laifukan da yawan su ya kai 79.

Ko bayan zabubukan rundunar ta ce an samu wasu mutane da ke fakewa da samun nasarar zabe, wajen yin murna sai su rika aikata laifuka duk da yake ba yawun jam'iyun su, suke yin hakan ba.

'Yan sandan Najeriya yayin wani atisaye (Facebook/Rundunar 'yan sandan Najeriya)
'Yan sandan Najeriya yayin wani atisaye (Facebook/Rundunar 'yan sandan Najeriya)

Wannan batun a cewar kwamishinan ‘yan sanda Muhammad Usaini Gumel sun yi bincike akan sa kuma yanzu haka batun na gaban kuliya.

Kwamishinan ya ce akwai wasu misalai na irin wadannan matsalolin da suka samu kamar a karamar hukumar Tureta inda wasu suka harbe matar wani mutum a idon ta ta amfani da danko a lokacin da suke murna, yace akwai mamaki masu murna su rike makami kamar danko har suna harbin mutane.

Hakama a cikinsu an samu ire-iren wadannan matsalolin kuma kwamishinan yace yanzu haka suna farautar wasu da ke da hannu ciki.

'Yan sandan Najeriya yayin kaddamar da rundunar wanzar da zaman lafiya a jihar Enugu (Twitter/@PoliceNG)
'Yan sandan Najeriya yayin kaddamar da rundunar wanzar da zaman lafiya a jihar Enugu (Twitter/@PoliceNG)

Yanzu da yake hukumar zaben Najeriya ta tsayar da 15 ha Aprilu a zaman ranar kammala zabubukan da basu kammala ba, a jihohin kasar, kwamishinan ‘yan sanda yace rundunar tare da sauran hukumomi na tsaro ba zasu yi kasa a guiwa ba wajen dakile duk wani yunkuri na tayar da fitina.

Da ma tun kafin gudanar da zabubukan da aka yi a 25 ga Fabrairu da na 18 ha Maris, wasu ‘yan siyasa sun amince da wanzar da zaman lafiya tsakanin magoya bayan su, kafin zabe, lokacin zabe da bayan zabe, kuma jami'an tsaron Najeriya sun lashi takobin tabbatar da hakan.

Saurari cikakken rahoton cikin sauti:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:15 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG