Wasu hare hare da aka kai a wasu yankunan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya, sun yi sanadiyar mutane da dama.
Rahotanni sun ce, daga cikin wadanda hare-haren suka rutsa da su a tsakiyar makon nan a yankin karamar hukumar Birnin Magaji, akwai manoma da ke kan aiki a gonakinsu a lokacin da harin ya auku.
Wasu majiyoyi sun bayyana cewa, wasu mahara dauke da muggan makamai suka far wa manoma a yankin Garin Haladu kamar yadda jaridar Premium Time ta ruwaito.
Mazauna yankin sun fadawa jaridar cewa, maharan sun isa yankin ne da misalin karfe daya na rana, suka bude wuta akan wasu matasa da ke aikin dankalin Hausa a gonakinsu da ke Garin Haladu.
Akalla matasa 12 suka rasa rayukansu a wannan hari.
“Matasa da dama daga unguwar Nasarawa Godal, sun garzaya zuwa Garin Haladu domin kai dauki, inda aka kashe hudu daga cikinsu, amma sai a ranar Alhamis aka gano gawarwakinsu.” In ji wani mazaunin garin da ya gana da Premium Times, wanda kuma ya nemi da kada a bayyana sunansa.
Majiyar ta kara da cewa, a Garin Kaka, mutane 9 maharan suka kashe.
Rikicin yankin Zamfara mai fama da hare-haren ‘yan bindiga, ya zama babban al’amari a Najeriya, wanda ya sa hukumomi tura karin dumbin jami’ai domin tunkarar ‘yan bindigar, amma duk da haka ana ci gaba da samun daidaikun hare-hare.
Bayanai da ke fitowa a ‘yan kwanakin nan, sun nuna cewa jami’an tsaro na samun nasara akan maharan, tun bayan da aka kaddamar da wani shirin tarwatsa 'yan bindigar da ake kira "Operation Dirar Mikiya," amma masu fafutukar kare hakkin bil Adama da mazauna yankin suna ci gaba da kiran neman dauki.
Facebook Forum