Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sabon Faifan Boko Haram


Iyayen Maida Yakubu yarinyar da tayi magana a faifan bidiyon da wani bangaren Boko Haram ya fitar
Iyayen Maida Yakubu yarinyar da tayi magana a faifan bidiyon da wani bangaren Boko Haram ya fitar

Wani bangaren Boko Haram a karkashin shugabancin Abu Muhammad Asshakawai ya nuna wasu 'yan matan da kungiyar ta sace fiye da shekaru biyu da suka gabata har ma wata Maida Yakubu ta mika rokonsu

A cikin faifan da wani bangaren kungiyar Boko Haram ya fitar, domin kungiyar ta rabu ukku, an nuna wasu 'yan matan Chibok tare da ba wata Maida ta mika rokonsu domin su samu kubuta.

Bangaren dake karkashin shugabancin Abu Muhammad Asshakawi tace suna rike da 'yan matan kuma duk barazanar gwamnatin Buhari tare da abun da ya kira karyar da gwamnatin ke yi ba zasu iya kubutar da 'yan matan ba idan ba'a biya masu nasu bukatun ba.

Shugaban yace dole ne gwamnatin Buhari ta sako masu 'yan uwansu dake tsare a Borno, Abuja da Legas kafin su sako 'yan matan. Kin yin hakan zai kaiga rasa 'yan matan na har abada.

Yace sanadiyar harin bamamai da sojojin Najeriya ke kaiwa kansu har wasu 'yan matana sun halaka. Baicin hakan, 'yan mata fiye da arba'in sun yi aure.

Uwar Maida tana kallon bidiyon
Uwar Maida tana kallon bidiyon

Iyayen Maida sun ga faifan kuma mahaifinta yace ya ga diyar tasa ta rame

Ga bidiyon na Boko Haram, bangaren Abu Asshakawi.

Sabon Bidiyon Boko Haram
please wait

No media source currently available

0:00 0:11:25 0:00

Wata manhaja mai saukaka wahalar samun gidan abinci na halal ga Musulman dake zaune a kasashen Turai
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:21 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG