Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sanata Maina Maji Lawal Ya Musanta Yawan Mutanen Da Su Ka Mutu A Baga


Wasu mata da yara tsayer a jikin wani gidan da ya kone a Baga, Jihar Borno
Wasu mata da yara tsayer a jikin wani gidan da ya kone a Baga, Jihar Borno

Sanatan mai wakiltar arewacin Borno, ciki har da garin Baga, yayi ikirarin cewa mutane akalla 228 ne suka mutu a wannan tashin hankali na makon jiya

Tsohon gwamnan Jihar Borno, kuma sanata mai wakiltar Borno ta Arewa a majalisar dattijan Najeriya, Maina Maaji Lawal, yace mutane akalla 228 ne aka kashe a lokacin kazamin tashin hankalin da aka yi makon jiya a garin Baga.

Da yake zantawa da 'yan jarida a Maiduguri, bayan wata ziyarar gani da ido da ya kai zuwa garin Baga, sanatan yace ya tarar da mutane cikin mummunan hali na jinkai, inda yace tantuna guda biyu kadai na hukumar agajin gaggawa ta Najeriya, NEMA, ya gani a wurin, kuma mutane su na kwana tare da wuni a filin Allah saboda sun rasa matsuguni,

Ya kuma ce gidaje akalla dubu 4 ne aka kona su kurmus a wannan gari da ya shahara wajen kamun kifi a bakin iyakar Najeriya da Chadi.

Wannan adadi na sanatan, ya sha bambam da mutane 36 da hukumomin sojan Najeriya suka ce an kashe, da kuma 187 da kafofin labarai suke ambata daga bakin wani jami'in gwamnatin jihar Borno.

Ga rahoton wakilinmu Haruna Dauda Biu daga Maiduguri.

Rahoton Haruna Dauda Kan Hirar Sanata Maina Ma'aji Lawal - 3:35
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:35 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG