Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Saudi Arabia Da Kawayen Sun Baiwa Kasar Qatar Waadin Sa'o'i 48


HAJJ 2016
HAJJ 2016

Kasar Saudiyya da kawayenta da suke rikici ta fuskar difilomasiyya da Qatar, yau Litinin, suka kara wa'din da suka baiwa Qatar da sa'o'i 48 ta cika sharudda da suka gindaya mata.

Jiya Lahadi Kuwait, wacce take shiga tsakani domin kawo karshen rikicin cikin lumana, ta nemi a kara wa'adin, jim kadan kamin karshen wa'adin farko.
Sanarwar da kamfanonin dillancin labaran Kuwait da Saudiyya suka bayar a sanyin safiyar yau Litinin din nan duk sun tabbatar da cewa an kara wa'adin har zuwa karshen yau Litinin.
Kasashen Saudiyya, da hadaddiyar daular kasashen Larabawa, da Bahrain, da Masar sun yanke huldar difilomasiyya da kasuwanci da Qatar ranar 5 ga watan Yuni, suna zargin gwamnatin Qatar da goyon bayan ta'addanci.
Qatar ta musanta zargin da wadan nan kasashe suka yi mata, tace zargin bashi da wani tushe. Ministan harkokin wajen wannan karamar kasa dake yankin na Gulf, Sheikh Mohammed bin Abdulrahman al-Thani, yace sharuddan da Saudiyya da kawayenta suke gindaya mata, da suka hada da janye sojojin Turkiyya daga kasar, da rufe tashar talabijin ta al-Jazeera da tauye dangantakar ta da Iran, suna da wuya ta mutunta su ba tareda ta sadaukar da diyaucinta ba.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG