Kasar Saudiyya, ta kasance daya daga cikin wasu kasashen da suka kaurace wa wani taron kwanaki hudu da aka shirya za a yi a Kuala Lumpur, domin duba kalubalen da duniyar Musulunci ke fuskanta.
Firai Ministan Malaysia, Mahatir Mohamad ne ya shirya taron, inda ake so a tattauna kan batutuwa kamar na halin da Musulmin Uighur ke ciki a Lardin Xinjian da ke China.
Ana zargin hukumomin China da tsare miliyoyin ‘yan kabilar ta Uighur wadanda Musulmi ne, a wasu sansanoni ba da son ransu ba, zargin da Chinan ke musantawa.
Ita dai Saudiyya ta kaurace wa zaman ne saboda a cewarta, taron na gudana ne, ba tare da yawun kungiyar kasashen Musulumi ta OIC ba, wacce ke da hedkwata a Jedda.
A jiya Laraba kungiyar ta OIC, ta fitar da wata sanarwa, inda ta ce, irin wadannan taruka na kassara ayyukanta da na Musulunci.
An dai tsara Firai Ministan Pakisatan, Imran Khan zai halarci taron, amma ya janye bayan da Saudiyya ta tursasa shi da kada ya je, kamar yadda rahotanni suka bayyana.
Sai dai kasashe irinsu Iran, Turkiyya, Qatar, wadanda ba sa dasawa da Saudiyya, na halartar wannan taro.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum