Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shin Kasashen Afirka Na Iya Kafa Takardar Kudi Daya?


Wasu shugabannin kasashen Afirka a taron kolinsu na wannan shekarar da suka yi a birnin Addis Ababa dake kasar Habasha
Wasu shugabannin kasashen Afirka a taron kolinsu na wannan shekarar da suka yi a birnin Addis Ababa dake kasar Habasha

Bayan shugabannin kasashen Afirka sun kammala taron kolinsu na wannan shekarar wasu cikinsu da manyan 'yan kasuwa na kiran nahiyar Afirka ta samar da takardar kudi daya da kuma kawar da batun yin anfani da biza wajen yin balaguro tsakanin kasashensu.

Tun kafin wannan kiran tsohon shugaban Najeriya Chief Olusegun Obasanjo ya kira kasashen Afirka su samar da takardar kudi ta bai daya, farko a kasashen yammacin Afirka kana da Afirkan baki daya.

Masana tattalin arziki sun kalli maganar daban. Dr. Dauda Muhammad Kontagora wani masanin tattalin arziki yace kasashe kamar na yammacin Afirka na iya taimakawa juna akan shige da fice domin tattalin arzikinsu ya habaka amma yin kudi na bai daya nada nashi matsalolin.

Yace kwazon tattalin arzikin kasashe ba iri daya ba ne. Wata kasa ta fi wata kasa kwazo. Haka ma wata kasa ta fi wata kasa karfin tattalin arziki. Idan aka yi masu kudi na bai daya akwai kasashen da zasu cutu.

Shi ma Alhaji Aliko Dangote ya bayyana bukatar an kawo karshen yin anfani da biza saboda balagiro daga wannan kasa zuwa waccan. Kawai da biza sai bada sukunin yin kasuwanci tsakanin kasashe.

Matakan da wasu kasashe ke dauka na tsaro ko na tattalin arziki su kan shafi makwaftansu. Misali matakin da Najeriya ta dauka na hana shigo da motoci da shinkafa ta kan iyakokin kasa ya yiwa tattalin arzikin Banin da Togo rauni.

A saurari rahoton Babangida Jibrin.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG