Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Muhammadu Buhari Ya Sauke Manyan Sakatarori


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sallami manyan sakatarorin ma’aikatun gwamnatin tarayya daga mukamansu bayan ganawa da yayi da su a fadar gwamnati.

Duk da yake shugaban kasar bai bayyana dalilin sauke sakatararorin ma’aikatun gwamnatin tarayya goma sha bakwai ba, masu fashin baki sun bayyana cewa, hakan bata rasa nasaba da yunkurin shugaba Buhari na yaki da cin hanci da rashawa, kasancewa ana zargin irin wadannan sakatarorin da hada baki wajen yin rubda ciki da dukiyar talakawa.

Ana ganin sallamar manyan sakatarorin a wani yunkurin nisanta wannan gwamnatin da jami’an gwamnati da ake zargi da yiwa dokokin aikin gwamnatin karan tsaye da kuma cin karensu ba babbaka.

Gobe ne dai ake kyautata zaton shugaba Buhari zai rantsar da ministoci wadanda kawo yanzu ba a tantance ma’aikatu da za a tura su ba.

Ga bayanin wakilin Sashen Hausa a Abuja, Umar Faruk Musa

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:02 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG