Shugaban Amurka Donald Trump ya sanyawa Iran sabbin takunkumi, sa’o’i bayan da shugaban kasar Iran, ya ce ya janye daga yarjejeniyar da aka kula tsakanin kasashe shida, kan makamin nukiliyanta.
A jiya Laraba Trump wanda ya yi amfani da ikon da doka ta ba shi na kashin kansa, ya ce, zai saka sabbin takunkumi kan nau’ukan kayayyakin da suka hada har da na karafa, wadanda suna daga cikin kayayyakin da suke samawa kasar kudaden shiga.
Takunkumi da Amurka ta sanya, a kan man Fetur din kasar ta Iran, wanda shi ne babban hanyar samun kudin shigar kasar, ya yi mummunan tasiri, a kan tattalin arzikinta.
Fannin sarrafa karafa, ya kasance wata babbar hanya da kasar ke samun kudaden.
Shugaba Trump ya ce, "saboda matakin da muka dauka, yanzu gwamnatin Iran, tana kokarin neman kudin da za ta zuba a fannin, daukan nauyin ayyukan ta'addanci, yayin da tattalin arzikinta, ke ci gaba da shiga cikin matsanancin hali."
Tada jijiyar wuya, da ake yi, tsakanin Iran da Amurka, ya yi kamari a cikin ‘yan kwanakin nan.
Za ku iya son wannan ma
-
Maris 26, 2023
Mataimakiyar Shugaban Amurka Kamala Harris Ta Isa Ghana
-
Maris 21, 2023
Saudiyya Ta Ce Ranar Alhamis Watan Azumi Zai Kama
-
Maris 17, 2023
Kotun ICC Ta Ba Da Izinin Kama Putin
-
Maris 13, 2023
Shugaba Buhari Ya Taya Xi Jinping Murnar Sake Lashe Zabe
Facebook Forum