Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Mulkin Sojan Nijar Ya Rusa Kananan Hukumomi



Shugaban majalissar sojojin juyin mulkin jamhuriyar Nijer Janar Abdourahamane Tchinai
Shugaban majalissar sojojin juyin mulkin jamhuriyar Nijer Janar Abdourahamane Tchinai

“An soke majalisun kananan hukumomi da na kananan hukumomi da na yanki,” in ji rahoton ba tare da bayar da wani bayani ba.

Shugaban gwamnatin mulkin sojan Nijar ya ba da umarnin rusa dukkan kananan hukumomi tare da dora wani jami'in soja a matsayin mai kula da babban birnin kasar, kamar yadda kafafen yada labaran kasar suka sanar.

Janar Abdourahamane Tiani wanda ya hambarar da zababben shugaban kasar a wani juyin mulki a watan Yulin da ya gabata, ya sanya hannu kan dokar rusa majalisun kananan hukumomi da na shiyya-shiyya da aka zaba na karshe a shekarar 2020, Tele Sahel ya rawaito.

“An soke majalisun kananan hukumomi da na kananan hukumomi da na yanki,” in ji rahoton ba tare da bayar da wani bayani ba.

Wata doka ta biyu da gidan rediyon gwamnati ya sanar, ya sanar da sunayen sojoji, ‘yan sanda da jami’an gwamnati wadanda za a dora su a kan kananan hukumomin.

An maye gurbin Oumarou Dogari magajin garin Yamai babban birnin kasar da wani kanar na soji.

Sojoji sun kwace kasar, daya daga cikin matalautan kasa a duniya a shekarar da ta gabata, yayin da take fuskantar barazanar masu jihadi.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG