Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabanin Tarayyar Turai Sun Yi Alkawari Taimakawa Italy da Libya Dakile Kwararar Bakin Haure


Wasu shugabannin Tarayyar Turai
Wasu shugabannin Tarayyar Turai

Shugabannin Tarayyar Turai sun yi alkawarin ba da karin kudade a jiya Alhamis, domin taimakawa Italiya da Libya wajen dakile kwararar bakin haure daga arewacin Afirka dake kokarin isa nahiyar ta turai.

“Mu na da kwakkwarar dama da zamu iya rufe hanyar nan ta tekun Meditareniya,” a cewar shugaban Majalisar kungiyar ta EU, Donald Tusk, yayin da yake ganawa da manema labarai a taron kolin da aka yi a Brussels.

Bayanin na Tusk na nuni ne da tsallaka tekun Meditareniya mai cike da hadari da bakin haure ke yi tsakanin Libya da Tsibirin Lampedusa da ke Italiya – mashigi na farko da bakin na haure ke isa a nahiyar ta turai.

Dubban mutane ne suke halaka yayin da suke kokarin tsallaka tekun a cikin jiragen kwalekwale marasa inganci, ko kuma idan masu safarar mutanen sun yasar da su akan tekun.

Hukumomin Italiya sun ce adadin bakin hauren da ke tasowa daga Libya ya ragu da kashi 20 cikin 100 a bana, tun bayan da suka hada kai da takwarorinsu na Libya wajen dakile kwararar bakin hauren.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG