Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojojin Afghanistan Sama Da 40 Sun Mutu


Sojojin Cadi na Ragargaza Boko Haram, Maris 05, 2015

Maaikatar harkokin tsaron Afghanistan ta bayyana cewa kusa sojoji sama 40 ne suka halaka sakamakon wani harin da 'yan taliban suka kai wa sojojin kasar.

Ministan harkokin tsaron kasar Afghanistan yace a kalla sojoji arba’in da hudu sun mutu a wani hari da mayakan Taliban suka kaiwa sansanin sojin kasar dake kudanci yau alhamis.

Sojoji tara suka ji rauni a harin da aka kai yau da asuba a sansanin dake Kandahar , yayinda wadansu shida suka bace. Ma’aikatar tace an kashe maharan Taliban goma.

A sanarwar da kungiyar Taliban ta bayar da ta dauki alhakin harin, tace sojoji sittin aka kashe.
Sun fara aukawa sansanin ne tare da kai harin kunar bakin wake a wata mota daga nan wani gungun mayaka ya kutsa sansanin suna ci gaba da bude wuta.

Wannan ne hari na uku mafi muni da kungiyar Taliban ta kaiwa cibiyoyin tsaro wannan makon, dukansu kuma da salo daya. A kalla mutane hamsin da biyu aka kashe a harin da aka kai wata cibiyar horarda ‘yan sanda dake birnin Gardez ranar Talata, aka kuma sake kai wani harin ranar a lardin Ghazni dake kudanci.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG