Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taraba: Majinyata Sun Fara Kokawa Game Da Yajin Aikin Likitoci


Ana duba yara a karamin asibiti dake kauyen Bagega a jihar Zamfara ta arewa maso yammacin Najeriya.
Ana duba yara a karamin asibiti dake kauyen Bagega a jihar Zamfara ta arewa maso yammacin Najeriya.

Yanzu haka yajin aiki da kananan likitocin Najeriya ke yi ya fara jefa majinyata cikin wani hali, sakamakon rashin samun kulawa lamarin da yakai cewa jami’an jinya ne kawai ke kula da marasa lafiyan.

Wadanda lamarin yafi shafa a yanzu sune majinyatan da basu da galihu na zuwa asibitocin kudi kamar yadda wasu majinyata a jihar Taraba arewa maso gabashin kasar suka koka.

Dakta Kefas Thomas, na daga cikin shugabanin kungiyar likitocin Najeriya a jihar Taraba, ya ce sun tsunduma wannan yajin aikin ne, biyo bayan shakulatin bangaro da suke zargin gwamnatin kasar na nuna musu na rashin biyansu hakkokinsu.

Da yake zantawa da manema labarai Dakta Thomsa, ya ce zasu ci gaba da yajin aikin har sai gwamnatin ta biya musu bukatunsu.

Suma dai shugabanin asibitoci sun koka da yajin aikin likitocin, Dakta Inusa Wuza, dake zama shugaban asibitin gwamnatin tarayya na FMC, Jalingo ya ce abin takaici ne, to amma suna kokarin lallabar likitocin.

Domin cikakken bayani saurari rahotan Ibrahim Abdul’aziz.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:30 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG