Wasu daga cikin 'yan takarar gwamna karkashin jam’iyar APC a jihar Taraba, sun musanta batun cewa an sasanta tsakaninsu, kuma sun yi mubaya'a ga dan takarar da ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyar, Sani Abubakar Danladi.
Shugaban jam’iyar jihar Taraba, Farfesa Sani Yahya, wanda na daya daga cikin 'yan takara takwas da suka kai kukansu ga uwar jam’iyar APC, ya ce sun yi mamaki da wasu ke yada cewa sun janye a fafutukar da suke yi kan batun takarar.
Sai dai kuma wannan na zuwa ne yayin da tuni jam’iyar ta fara gangami yakin neman zabe.
A wata hira da ya yi Muryar Amurka, tsohon mukaddashin gwamnan jihar, Sani Abubakar Danladi, wanda shi ne dan takarar gwamna a jam’iyyar ta APC a Taraba, ya yi kira ga sauran 'yan takara da su zo a hada kai domin a ceci jihar.
Saurari cikakken rahoton Ibrahim Abdulaziz domin karin bayani:
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 03, 2023
'Yan Kasashen Waje Masu Saka Ido A Zabe Sun Fara Isowa Najeriya
-
Fabrairu 03, 2023
Kotu Ta Raba Auren Diyar Ganduje
-
Fabrairu 03, 2023
Wani Bene Mai Hawa Uku Ya Rushe a Abuja
-
Fabrairu 02, 2023
Al'ummar Najeriya Sun Shigar Da Karar Kamfanin Shell A Kotu A Landan
Facebook Forum