Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taron Kolin Shugabannin Kasahe Kan Matsalolin Yan Gudun Hijira


Shugabannin kasashen duniya.
Shugabannin kasashen duniya.

A yau ne shugabannin kasashen duniya dama suke kwamba a birnin Istambul na kasar Turkiyya don soma taron kolin nan da aka dade ana jira a yi don shimfida ingantattun hanyoyin tunkarar matsaloli masu alaka da al’amarin gudun hijira.

Wannan taron da aka soma a yau kuma za’a ci gaba da yinsa har zuwa Jumu’a, ana fatar zai fito da matakan da za’abi wajen shawo kan bala’ukkan dake yawan faruwa har suna haifarda gudun hijiran milyoyin mutane, sannan kuma da yadda za’a kare kasashe masu tasowa daga irin wadanan fitinnun.

Shugabannin kasashe fiyeda 125 ke halartar wannan taron a kasar ta Turkiyya wacce ita kanta ke cikin jin jiki sosai a sanadin matsalar dubban ‘yan gudun hijiran dake kwarara zuwa cikin Nahiyar Turai.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG