Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taron Tunawa Da Mazan Jiya Da Suka Yaki Dakarun Nazi


Shugaban Amurka Donald Trump a taron shugabannin duniya a birnin Portmouth
Shugaban Amurka Donald Trump a taron shugabannin duniya a birnin Portmouth

Taron shugabannin duniya a birnin Portmouth domin tunawa da dakarun hadakar kasashen nahiyar turai da suka yi taron dangi suka kuma samu nasara akan sojojin Nazi.

Shugaban Amurka Donald Trump ya hadu da Firai ministar Birtaniya Theresa May da Firai ministan Canada Justine Trudeau da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da sauran shugabannin duniya a birnin Portmouth da ke kudancin Birtaniya, domin tunawa da dakarun hadakar kasashen nahiyar turai da suka yi taron dangi suka kuma samu nasara akan sojojin Nazi.

Taron ya kunshi kade-kade da karanto tarihin abin da ya faru a lokacin, ciki har da inda Shugaba Trump ya karanta addu’ar da tsohon shugaban Amurka Franklin Roosevelt ya taba karantawa ga masu sauraren rediyo, bayan da aka fara mamayar sojojin na Nazi a shekarar 1944.

Ita ma Sarauniyar Ingila Elizabeth ta 2 ta shiga cikin taron tare da tsoffin dakaru da suka taka rawa a wannan rana, wacce ake wa lakabi da D-Day.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG