Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tawagar Majalisar Dinkin Duniyar Na Ziyara a Jamhuriyar Nijar


Tawagar Amina Mohammed a Nijar
Tawagar Amina Mohammed a Nijar

Mataimakiyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed, ta fara ziyara a Jamhuriyar Nijar, domin tattauna hanyoyin magance matsalolin mata a fannoni da dama kamar batun auren wuri da rashin baiwa mata dama a harkokin siyasa.

Tawagar Amina Mohammed da ta samu rakiyar ministan harkokin wajen Sweden da shugabar kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya (MDD) sun gana da sarakunan gargajiya da shugabannin addinai da kuma kungiyoyin mata.

Haka kuma tawagar ta ziyarci fadar shugaban kasa inda suka gana da shugaba Muhammadu Isuhu.

A cewar Aisha Mohammed, ta kai wannan ziyara ne domin tattaunawa da shugaban kasa da masu ruwa da tsaki kan harkokin mata, da kuma baiwa mata damar taka rawa a fanoni daban-daban.

MDD na kokarin taimakawa wajen wayar da kai ga gwamnatoci kan kula da matsalolin mata da suka hada da yin auren wuri da kuma baiwa mata damar rike mukaman gwamnati da shiga harkokin siyasa.

Tawagar Aisha Muhammad a Nijar
Tawagar Aisha Muhammad a Nijar

Tawagar Amina dai ta je karkarar Maradi, domin ganewa idanunta zahirin halin da mata ke ciki, a wani yunkurin tantance mizanin ayyukan da kungiyoyin da ke samun tallafin MDD ke gudanarwa akan maganar inganta rayuwar mata.

Domin karin bayani saurari rahotan Sule Muminu Barma.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:17 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG