Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Ya Dakatar Da Shugaban CBN


Godwin Emefiele (Hoto: Facebook/CBN)
Godwin Emefiele (Hoto: Facebook/CBN)

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da sanarwar dakatar da Mista Godwin Emefiele, gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) daga aiki nan take. 

Wannan mataki ya zo ne a sakamakon binciken da ake yi a ofishinsa da kuma yin gyare-gyare a fannin hada-hadar kudi na tattalin arzikin kasar.

Sanarwar da Daraktan Yada Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya Mista Willie Bassey ya fitar ta bayyana hakan.

Shugaban CBN, Godwin Emefiele
Shugaban CBN, Godwin Emefiele

A cewar sanarwar, shugaba Tinubu ya umurci Mista Emefiele da ya gaggauta mika ragamar mukaminsa ga mataimakin gwamna (Operations Directorate). Mataimakin gwamnan zai yi aiki a matsayin mukaddashin gwamnan babban bankin kasa CBN har sai an kammala bincike da aiwatar da gyare-gyaren da aka tsara.

XS
SM
MD
LG