Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Ya Nada Wike Ministan Abuja, Badaru Ministan Tsaro


Tinubu, hagu, Wike, dama (Hoto: Facebook/Asiwju Bola Ahmed Tinubu)
Tinubu, hagu, Wike, dama (Hoto: Facebook/Asiwju Bola Ahmed Tinubu)

Fitar da sanarwar ma'aikatun da ministocin za su jagoranta na zuwa ne bayan da majalisar dattawa ta kammala tantance su makonnin da suka gabata.

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya rabawa ministoci 46 mukamai bayan da majalisar dattawa ta kammala tantance su a kwanakin baya.

Tinubu ya nada tsohon Gwamnan jihar Rivers Nyesom Wike a matsayin Ministan Babban birnin Tarayya na Abuja.

Kazalika Tinubu ya nada Festus Keyamo a matsayin Ministan sufurin sama.

Tsohon gwamnan Jigawa Mohammad Badaru Abubakar
Tsohon gwamnan Jigawa Mohammad Badaru Abubakar

Tsohon gwamnan jihar Jigawa Muhammadu Badaru ne zai jagoranci ma'aikatar tsaro a cewar kafafen yada labaran Najeriya.

Ga sauran jerin ministocin da Tinubu ya rabawa mukamai:

Ministar raya al’adu da Ggrgajiya – Hannatu Musawa

Karamin Ministan Tsaro – Bello Matawalle

Karamin Ministan Ilimi – Yusuf T. Sunumu

Ministan Gidaje da raya Alkarya – Ahmed Dangiwa

Karamin Ministan Gidaje da raya Alkarya – Abdullahi Gwarzo

Ministan Kasafin kudi da Tsara Tattalin Arziki – Atiku Bagudu

Karamar Ministan Birnin Tarayya – Mariya Mairiga Mahmud

Tsohon Gwamnan Zamfara Bello Matawalle (Facebook/Zamfara Dep Governor)
Tsohon Gwamnan Zamfara Bello Matawalle (Facebook/Zamfara Dep Governor)

Karamin Ministan kula da albarkatun kasa da na ruwa da tsaftace muhalli – Bello Goronyo

Ministan Noma da Samar da abinci – Abubakar Kyari

Ministan Ilimi - Tahi Momoh

Ministan Cikin gida – Sa’idu Alkali

Ministan harkokin wajen – Yusuf Tuggar

Ministan Tsara harkokin lafiya da al’amuran ci gaba – Ali Pate

Ibrahim Geidam
Ibrahim Geidam

Ministan Hukumar ‘yan sanda – Ibrahim Geidam

Karamin Ministan Bunkasa harkokin Karafa – U. Maigari Ahmadu.

Ministan Sadarwa da tattalin arzikin zamani – Bosun Tuani

Karamin Ministan muhalli – Ishak Salako

Ministan Kudi da shirya tsare-tsare tattalin arziki – Wale Edun

Ministan kula da teku da albarkantu – Bunmi Tunji-Ojo

Ministan kula da wutar lantarki – Adebayo Adelabu

Karamin Ministan lafiya da kula da walwala – Tunji Alausa

Ministan kula da albarkatun kasa – Dele Alake

Ministan kula da fannin yawon bude ido – Lola Ade-John

Tsohon gwamnan Ebonyi David Umahi
Tsohon gwamnan Ebonyi David Umahi

Ministan Sufuri – Adegboyega Oyetola

Ministar kula da ma’akatu, kasuwanci da saka hannun jari – Doris Anite

Ministan kirkire-kirkire, kimiyya da fasaha – Uche Nnaji

Karamin Ministan kwdago da daukan ma’aikata – Nkiruka Onyejeocha

Ministar Mata – Uju Kennedy

Ministan Ayyuka – David Umahi

Ministan Matasa – Abubakar Momoh

Ministar ayyukan jin-kai da yaki da talauci – Betta Edu

Karamin Ministan albarkatun Gas – Ekperipe Ekpo

Karamar Ministar Albarkatun mai – Heineken Lokpobiri

Ministan Wasanni – John Enoh

Karamin Ministan noma - Aliyu Sabi Abdullahi

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG