Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Trump, Biden Na Jimamin Rasuwar Ginsburg


Marigayiya, Mai Shari'a Justice Ruth Bader Ginsburg ta Kotun Kolin Amurka (AP…
Marigayiya, Mai Shari'a Justice Ruth Bader Ginsburg ta Kotun Kolin Amurka (AP…

Ana ci gaba da nuna alhini dangane da rasuwar Mai Shari’a a kotun kolin Amurka Justice Ruth Bader Ginsburg, wacce ta rasu a ranar Juma’a tana mai shekara 87.

Rasuwar Ginsburg, wata dama ce da Shugaba Donald Trump ya sake samu a karo na uku, ta fadada rinjayen masu ra’ayin mazan jiya a kotun kolin Amurka, yayin da wasu ke ganin kasar na fama da rarrabuwar kawuna, a kuma daidai lokacin da ake tunkarar zabe kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Associated Press ya ruwaito.

Ginsburg ta yi “rayuwa mai ban mamaki, babu abin da za a iya cewa, illa a ce, mata ce mai ban mamaki,” shugaba Trump na jam’iyyar Republican ya fadawa manema labarai bayan da ya samu labarin rasuwar bayan kammala wani gangamin yakin neman zabe a jihar Minnesota, inda ya kara da cewa yana mai cike da bakin cikin wannan rashi.

A kuma wata sanarwa da ya fitar, shugaban ya kara da cewa, Amurka, “na alhinin rashin wata jaruma a fannin shari’a.”

Ana shi bangaren, dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar Democrat Joe Biden, ya kwatanta marigariyar a matsayin wacce “ta tsaya tsayin daka ba tare da nuna tsoro ba a fafutukar kare hakkin kowa da kowa, yana mai cewa irin akidar da ta tsaya akai, za ta ci gaba da yin tasiri a fannin shari’a na wani tsawon lokaci.

Tun dai a shekarar 1993 aka zabi Ginsburg a matsayin daya daga cikin Alkalan kotun kolin Amurkan.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG