Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsohon Shugaba Boubacar Keita Ya Koma Gida


Tsohon shugaban Mali, Boubacar Keita

Tsohon Shugaban kasar Mali Ibrahim Boubakar Keita ya koma mazauninsa a Bamako babban birnin Kasar a yau Juma’a, kwana daya bayan da aka sako shi daga wani sansanin soja a Kita. 

Kwamitin sojan da ke Mulki a kasar da ake kira NCSP a takaice ya tsare Keita a lokacin da aka yi juyin mulki a kasar a makon da ya gabata, inda Keita ya sanar da cewa ya yi murabus jim kadan bayan aukuwar lamarin.

Kanal Ismael Wague
Kanal Ismael Wague

A lokacin da ya ke tsare, an bada rahoton cewa Keita ya ce ba tilasta ma shi aka yi ya sauka daga kan karagar mulki ba, kuma ba ya so ya koma, amma ya na so a koma wa tsarin dimokradiyya cikin sauri.

Majalisar Dinkin Duniya, tare da kungiyar kasashen yammacin Afrika ta ECOWA, ne suka bukaci a saki Keita, wanda kuma ake kira IBK a takaice.

Facebook Forum

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG