Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu Iyaye Sun Mayar Da Martani Game Da Zargin Mikawa 'yan Boko Haram 'ya'yansu


Yara a wani sansanin 'yan gudun hijira
Yara a wani sansanin 'yan gudun hijira

Wasu iyaye a birnin Maiduguri jihar Borno, arewa maso gabashin Nigeria, sun maida martani ga zargin da rundunar soja tayi cewa, wasu iyaye da kansu suke baiwa yan Boko Haram 'ya'yansu.

Wasu magidanta a jihar Borno, arewa maso gabashin Nigeria sun mayar da martani ga zargin da hafsan sojojin Nigeria ya yi cewa, wasu iyaye da kansu, suke baiwa 'yan kungiyar Boko Haram 'ya'yansu domin aiwatar da hare-haren kunar bakin wake.

Kusan dukkan wadanda suka bayyana ra'ayinsu ga wakilin Sashen Hausa Haruna Dauda biyu ba su amince da wannan zargin ba.

Misali daya daga cikin mutane ya ce, sai da idan "mutum mahaukaci" ne zai dauki dansa ko 'yarsa ya bai wa 'yan kungiyar Boko Haram domin a yi amfani da su wajen kai hare-haren kunar bakin wake.

Saurari rahoton Haruna Dauda Biu domin jin karin bayani:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:51 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG