WASHINGTON D C —
A birnin Beirut, dubban mutane ne suka fito yau Lahadi don nuna goyon bayansu ga shugaban kasar Lebanon.
Jama’ar sun gudanar da gangamin ne a kusa da fadar shugaba Michel Aoun dake kudu maso gabashin birnin Beirut.
Nuna goyon bayan ga Aoun na nuna adawa da zanga zangar da wasu ‘yan Lebanon suka fara a fadin karamar kasar dake yankin tekun bahar rum a watan da ya gabata, suna neman a yi garambawul a siyasar kasar da ake nuna wariya.
Masu zanga zangar sun kuma dora laifin cin hanci da rashawa da suka yi yawa sosai, da kuma rashin ayyukan raya al’umma akan gwamnatin kasar.
Ko da yake, ana sa ran gudanar da zanga zangar kin jinin gwamnati yau Lahadi da yamma a tsakiyar birnin Beirut.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum