Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wayar Salula Ta Kashe Kasuwar Jarida a Adamawa


Kasuwar jarida ta shude a Adamawa
Kasuwar jarida ta shude a Adamawa

Masu sana’ar sayar da jaridu a Najeriya da ake kira Vendors a turance, na kokawa game da matsalolin da suke fuskanta a yanzu na rashin kasuwa sanadiyar wayar salula da yanar gizo,lamarin da ke jefa su cikin wani mawuyacin hali.

A baya dai kafin soma amfani da kafofin sadarwa na internet, sana’ar sayar da jarida, sana’a ce da akan yi rububin shiga.

Sai dai da alamun ba haka lamarin yake ba a yanzu, inda, masu sana’ar sayar da jaridun ke kokawa game da rashin kasuwa musamman a wannan lokaci.

Malam Ali Muhammad wani dattijo ne da ya shafe fiye da shekaru 30 da uku yana sana’ar sayar da jarida a Najeriya,ya ce, yanzu sun zama yan kallo,biyo bayan bullowar harkar jarida ta kafar sadarwa, wato internet.

Malam Adamu Idris, tsohon mai sai da jarida ne a Yola, jihar Adamawa, ya ce yanzu babu batun yan free-readers,tun da yawancin jama’a na da wayar salula.

Free-readers, su e mutane da suke ba da dan wani kudi su samu damar karanta jarida a wajen masu sayar wa.

Su ma dai masana harkar jarida da yada labarai na danganta lamarin da koma baya ga harkar karance-karance da ake da shi a yanzu, baya ga rashin kudi da kuma wayar salula da yanar gizo da zamani ya zo da su.

Saurari rahoton Ibrahim Abdulaziz domin karin bayani kan wannan rahoto.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:29 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG